20 Agusta 2025 - 13:43
Source: ABNA24
Mahara Sun Kashe Masallata 27 A Wani Hari A Najeriya

'Yan bindiga sun kashe mutane 27 da suke sallah a wani mummunan hari da suka kai

Kamfanin Dillancin Labarain ƙasa da ƙasa Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: A wani hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a wani masallaci da ke jihar Katsina a arewacin Najeriya, wasu ‘yan bindiga sun mayar da wurin ibada wajen zubar da jini, inda suka kai hari a lokacin sallar asuba, inda suka kashe mutane akalla 27 tare da jikkata wasu da dama a juya talata.

Shaidu sun ce, kwatsam maharan sun shiga masallacin da ke wani kauye mai nisa a yankin Malumfashi inda suka bude wuta kan masu ibadar da ba su da kariya. A ‘yan makonnin da suka gabata ‘yan bindiga na karuwa a yankin arewaci da tsakiyar Najeriya, kuma duk da hare-haren da sojoji ke kaiwa, gwamnati na ci gaba da fafutukar ganin ta shawo kan matsalar rashin tsaro da kuma kare fararen hula.

Jami’an lafiya biyu a Najeriya sun ce akalla mutane 27 ne suka mutu tare da jikkata wasu da dama a wannan hari da wasu ‘yan bindiga suka kai a wani masallaci a jihar Katsina da ke arewacin Najeriya a ranar Talata.

Mazauna yankin sun ce wasu ‘yan bindiga sun kai farmaki masallacin ne a wani kauye mai nisa a yankin Malumfashi da misalin karfe 4 na safe agogon GMT a daidai lokacin da al’ummar musulmi suka taru domin yin sallah tare da bude wuta kansu.

Kawo yanzu dai babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai harin.

Tun da farko dai kafafen yada labarai na Najeriya sun ruwaito a farkon watan Satumba cewa an kashe wasu masu ibada guda bakwai bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari a wani masallaci a kauyen Saya-Saya da ke jihar Kaduna a yankin arewa maso yammacin kasar.

A karshen watan Agusta, wasu masallata 10 ne suka mutu inda wasu 30 suka jikkata sakamakon ruftawar wani masallaci a jihar Kaduna.

A watan Disambar shekarar da ta gabata ne wasu mahara dauke da makamai suka kai hari a wani masallacin karkara da ke yankin Fontua da ke arewa maso yammacin Najeriya a lokacin sallar magariba, inda suka harbe limamin masallacin tare da raunata wasu mutane 19 tare da yin garkuwa da wasu masallata 19.

Arewacin Najeriya dai ya fuskanci matsalar karancin abinci, inda aka kwashe shekaru 14 ana rikici tsakanin sojoji da kungiyoyin 'yan ta'adda inda 'yan ta'adda suka raba miliyoyin mutane da yawancinsu manoma da gidajensu.

Dukkan wadannan hare-haren suna faruwa ne yayin da jami'an hukumar Najeriya ke cewa tsaro na ci gaba da samuwa a Najeriya.

Tags

Your Comment

You are replying to: .
captcha